AI SAI NA ZAMA SHASHA HAWA BIYU
Wata rana shehu ya tafi ya kai alkamarsa wajen nika, da ya
isa gurin sai ya rika diban tafi dai dai daga buhunnan mutane yana zubawa a
buhunsa. Sai mai nika yace: lafiya kuwa, mene ne haka? Sai yace kai ni fa
shashasha ne, duk abin da hankalina ya shirya mini shi nakeyi. Sai mai nika
yace: to, idan kai shsha ne me yas baka debo alkama daga buhunka ka zuba a
buhunnan mutane? Sai yace : ai ni shashacina mai sauki ne, idan kuwa na aikata
abin da ka fada, sai na zama shashasha hawa biyu..
No comments:
Post a Comment